WAJIBI NE A KAN MALAMAI SU RIKA YIN UMURNI DA BIN UMURNIN ANNABI: Dr Ibrahim Jalo Jalingo

WAJIBI NE A KAN MALAMAI SU RIKA
YIN UMURNI DA BIN UMURNIN
ANNABI:
1. Wajibi ne a kan Malamai su tashi tsaye
su rika umurtan Mutane da bin umurnin
Manzon Allah mai tsira da amincin Allah cikin mas’alolin Aqidah, da Ibadah, da
kuma Mu’amalah.
2. A duk inda aka tarar da cewa umurnin
Manzon Allah ya saba da umurnin wani
mutum da ake girmamawa a cikin
Al’ummah, to dole ne a yi watsi da nasa umurnin a koma a bi umurnin shi Manzon
Allah mai tsira da amincin Allah. Wannan
shi ne Musulunci.
3. Al-Haafiz Bin Rajab ya ce a cikin
littafinsa: Al-Hikamul Jadiiratu Bil Izaa’ah
shafi na 12:- ((ﻓﺎﻟﻮﺍﺟﺐ ﻋﻠﻰ ﻣﻦ ﺑﻠﻐﻪ ﺍﻣﺮ ﺍﻟﺮﺳﻮﻝ ﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻴﻪ ﻭﺳﻠﻢ ﻭﻋﺮﻓﻪ ﺍﻥ ﻳﺒﻴﻨﻪ ﻟﻸﻣﺔ ﻭﻳﻨﺼﺢ ﻟﻬﻢ
ﻭﻳﺄﻣﺮﻫﻢ ﺑﺎﺗﺒﺎﻉ ﺃﻣﺮﻩ ﻭﺍﻥ ﺧﺎﻟﻒ ﺫﻟﻚ ﺭﺃﻱ ﻋﻈﻴﻢ ﻣﻦ
ﺍﻷﻣﺔ ﻓﺎﻥ ﺍﻣﺮ ﺭﺳﻮﻝ ﺍﻟﻠﻪ ﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻴﻪ ﻭﺳﻠﻢ ﺍﺣﻖ
ﺍﻥ ﻳﻌﻈﻢ ﻭﻳﻘﺘﺪﻯ ﺑﻪ ﻣﻦ ﺭﺃﻱ ﺍَﻱ ﻣﻌﻈﻢ ﻗﺪ ﺧﺎﻟﻒ
ﺃﻣﺮﻩ ﻓﻲ ﺑﻌﺾ ﺍﻷﺷﻴﺎﺀ ﺧﻄﺎ )). Ma’ana: ((Abin da yake wajibi a kan duk
wanda umurnin Manzon Allah mai tsira
da amincin Allah ya riske shi, ya kuma
gane shi, to sai ya bayyana shi ga
Al’ummah, ya yi musu nasiha, ya umurce
su da bin umurnin shi; ko da hakan ya saba wa ra’ayin wani babba daga cikin
Al’ummah; domin umurnin Manzon Allah
mai tsira da amincin Allah shi ya fi
cancantar a girmama a kuma yi koyi da
shi a kan ra’ayin dukkan wani wanda ake
girmamawa da ya saba wa umurninsa cikin sashin al’amura ta hanyar kure)).
Allah muke roko da Ya sanya
al’amuranmu cikin shiriya har kullum.
Ameen.

Leave a comment